Arewa Nexus

Arewa Nexus Kasance da mu domin samun sahihan rahotanni na dumi-duminsu a kan lokaci. 📰 We know your need

AREWA NEXUS: Matattarar ingantattun labarai, bincike mai zurfi, da al'amuran yau da kullum daga Arewacin Nijeriya da sassan duniya baki daya cikin harshen Hausa zalla.

Maryam Ibrahim Dan’azumi Ta Samu Kyautar Naira Miliyan 120!Maryam Ibrahim Dan’azumi daga Jihar Gombe, wadda ta zo ta ɗay...
19/08/2026

Maryam Ibrahim Dan’azumi Ta Samu Kyautar Naira Miliyan 120!

Maryam Ibrahim Dan’azumi daga Jihar Gombe, wadda ta zo ta ɗaya a sashen Tafsiri na mata na Hizb 60, ta samu kyautar Riyal 300,000 na Saudiyya, wanda ya yi daidai da kimanin Naira Miliyan 120,000,000 a kuɗin Najeriya.

Wannan babbar nasara ce ga Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.

Gomnatin Gwamna Babagana Umara Zulum ta bayyana cewa ta zuba jarin ₦15.29bn a fannin tallafin karatu na ɗaliban jihar tu...
19/08/2026

Gomnatin Gwamna Babagana Umara Zulum ta bayyana cewa ta zuba jarin ₦15.29bn a fannin tallafin karatu na ɗaliban jihar tun shekarar 2023, inda aka karkata sama da ₦8.61bn wajen ɗaukar dawainiyar karatun ƙasashen waje.

Gwamna Zulum ya sanar da hakan ne a taron maraba da ɗalibai 294 da s**a kammala karatunsu na ƙasashen waje a China, India, Egypt da Malaysia. Haka zalika, ya amince da fitar da kudi kimanin ₦2.65bn domin biya wa ɗalibai 158 da ke kan karatu bashin shekarar 2026.

Rarraban kudin tallafin ya kasu kamar haka:

₦8.61bn: Dawainiyar karatun ƙasashen waje.

₦3.83bn: Tallafin karatun ɗaliban cikin gida.

₦196.3m: Ayyukan gudanarwa na hukumar tallafin karatu.

Gwamnan ya jaddada cewa haɓaka ilimin matasa shi ne hanya mafi tabbas ta yaƙi da talauci da kangarar tsaro. Tare da hakan, ya sanar da ƙara adadin kudin tallafin karatu na ɗaliban cikin gida da kashi 100% (100 percent increase), inda ya umarci Kwamishinan Ilimi da Hukumar Scholarship da su aiwatar da hakan nan take.

Kwamishinan Ilimi, Engr. Lawan Abba Wakilbe, ya ƙara da cewa tsarin na kasashen waje ya maida hankali ne kan fannonin likitanci da injiniyari, kuma ɗalibai 171 sun kammala karatun digiri na biyu da na uku daga kasashen India da Malaysia guda 16 daga cikinsu da sakamako mai ninkayyar kyautatuwa (distinction).

“Ba Dan Guguwar Kwankwasiyya Da Ta Kawo Abba Ba, Ko Ni Na Fi Shi Daraja a Idon Mutane”— Hon. Tijjani Husaini Gandu, Dan ...
19/08/2026

“Ba Dan Guguwar Kwankwasiyya Da Ta Kawo Abba Ba, Ko Ni Na Fi Shi Daraja a Idon Mutane”

— Hon. Tijjani Husaini Gandu, Dan Takarar Majalisar Jiha a Mai Wakiltar Ƙaramar Hukumar Birni a Jam'iyyar NDC

DA DUMI-DUMI: Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci da a yi amfani da kudaden da Hukumar EFCC ta kwato zuwa asusun t...
19/08/2026

DA DUMI-DUMI: Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci da a yi amfani da kudaden da Hukumar EFCC ta kwato zuwa asusun tallafin lamunin ilmi na Najeriya (NELFUND).

Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan a yau Laraba yayin da yake wa manema labarai na Fadar Shugaban Ƙasa bayani bayan taron Majalisar Zartarwa (FEC).

Ministan ya kara da cewa Majalisar Zartarwa ta kuma amince da umarnin Shugaban Ƙasa na a karkatar da duk wata ribar hannun jari da ba a karɓa ba daga Capital Market Trust Fund da kuma Dormant Account Trust Fund zuwa NELFUND, domin ƙarfafa asusun wajen biyan kuɗaɗen lamunin ilimi da ake biyan dalibai.

19/08/2026

Saka mana hoton dan takarar ku a kwamen 👇🏻

Yau Za'a Rufe Musabaƙar Alƙur’ani  Ta Duniya Karo Na 46 A SaudiyyaƳan Najeriya huɗu sun shiga cikin waɗanda ke wakiltar ...
19/08/2026

Yau Za'a Rufe Musabaƙar Alƙur’ani Ta Duniya Karo Na 46 A Saudiyya

Ƴan Najeriya huɗu sun shiga cikin waɗanda ke wakiltar ƙasar wanda ake gudanarwa a Masarautar Saudiyya.

Daga cikinsu akwai Hafsa Muhammad Sada daga Jihar Kano, da Maryam Ibrahim Dan’azumi daga Jihar Gombe, Sauran wakilan su ne Abdullahi Asil daga Zamfara da Abdulmalik Muhammad Inuwa daga Taraba.

Surayya Aminu, wato Rayya Kwana Casa’in, jaruma ce ‘yar Kannywood wadda ta taso daga Kaduna bayan an haife ta a Legas. T...
19/08/2026

Surayya Aminu, wato Rayya Kwana Casa’in, jaruma ce ‘yar Kannywood wadda ta taso daga Kaduna bayan an haife ta a Legas.

Ta fara da sha’awar wasan kwaikwayo tun tana karama, ta yi karatu a fannin Mass Communication.

Ta shiga masana’antar fim, sannan ta samu babban suna bayan ta taka rawar Rayya a Kwana Casa’in.

Daga baya ta ci gaba da bayyana a fina-finai da shirye-shiryen Hausa daban-daban, ta kammala karatunta, ta shiga ayyukan al’adu kamar Kaduna Book & Arts Festival.

Kuma zuwa 2026 tana ci gaba da bunkasa sana’arta tare da fitowa a sabbin ayyuka kamar So Sanadi.

Yayin da take ci gaba da neman karin matsayi a masana’antar nishadi da rayuwa baki daya.

Malan Haruna mutumin da aka ka$hewa iyalinsa watanni kadan da s**a gabata a jiya ya tare da amaryar sa kuma a sabon gida...
19/08/2026

Malan Haruna mutumin da aka ka$hewa iyalinsa watanni kadan da s**a gabata a jiya ya tare da amaryar sa kuma a sabon gidansa da gwamna ya bashi.

Wani fata zaku masa?

19/08/2026

ZABEN 2027:

Yau da INEC ta bude yakin neman zabe shin wa zaku tallata a matsayin xabin ku?

Wai Me Ya Sa Ƴan Arewa S**a Lamincewa Tanimu Akawu Shi Kaɗai Ya Yi Tallar Tinubu Ba Tare Da Tsangwama Ba?Idan kun lura k...
19/08/2026

Wai Me Ya Sa Ƴan Arewa S**a Lamincewa Tanimu Akawu Shi Kaɗai Ya Yi Tallar Tinubu Ba Tare Da Tsangwama Ba?

Idan kun lura kusan duk wani ɗan fim da ya kinkimo tallar Tinubu ƴan Arewa ba sa raga masa, amma Tanimu Akawu ya zama shafaffe da mai a wajen ƴan Arewa.

Address

Maiduguri
Maiduguri

Telephone

+2348061552823

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Nexus posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Nexus:

Shortcuts

Share