29/04/2026
Kungiyar PDP a Matazu Ta Bukaci Babba Mazoji Ya Sake Tsayawa Takara
Wata kungiyar wayar da kan jama’a mai alaka da jam’iyyar PDP a karamar hukumar Matazu ta bukaci Hon. Zarahaddeen “Babba Mazoji” da ya sake tsayawa takara a zaben da ke tafe, bisa abin da ta bayyana a matsayin gudunmawar alheri da ya bayar a baya.
Kungiyar, wadda ke karkashin sunan PDP Political Awareness Movement Matazu, ta bayyana cewa Babba Mazoji ya gudanar da ayyukan jin kai da dama a lokacin da yake neman takarar Majalisar Dokokin Jihar Katsina a shekarar 2023.
A cewar kungiyar, gudunmawar da aka bayar ta shafi bangarori daban-daban da s**a hada da ilimi, lafiya, tsaro da walwalar al’umma, wanda a cewarsu ya taimaka wajen inganta rayuwar jama’a a yankin.
“Mun ga irin ayyukan alheri da ya gudanar, don haka muke kira gare shi da ya sake fitowa takara a kowace jam’iyya domin ci gaba da tallafa wa al’umma,” in ji wata sanarwa da kungiyar ta fitar.
Kungiyar ta kuma yi kira ga sauran ‘yan takara a yankin da su fito da irin gudunmawar da s**a bayar ga al’umma, domin bai wa jama’a damar tantance nagartarsu.
Ta jaddada cewa siyasa bai k**ata ta zama ta cin mutunci ko zagin juna ba, sai dai a mayar da hankali wajen bayyana ayyukan alheri da shirye-shiryen da za su amfani al’umma.
A karshe, kungiyar ta yi addu’ar Allah Ya zaba wa al’ummar Matazu shugabanni nagari masu kishin ci gaban jama’a.