Auwaluje Bawan Allah

Auwaluje Bawan Allah "Why does Allah not punish us for what we say ? Hell will be enough for them ! They will roast in it. What an evil destinations ! (Surat al-Mujadala:8)

13/05/2026

Ba kudi ba ne kadai yake kawo daraja.
Akwai dabi'u 10 da suke sa a girmama namiji a duk inda ya shiga.

1. Cika alkawari.
Namijin da maganarsa bata zama aiki... darajarsa zubewa take a idon mutane a hankali. Babu wanda zai fada masa, amma kowa zai daina yadda da shi.

2. Sarrafa zuciyarka.
Musamman fushi. Darajarka tana gushewa a daidai ranar da mutane s**a gane yadda zasu tayar maka da hankali cikin sauki.

3. Yin aiki a sirrance.
Duk yadda ka cika surutu akan abinda kake son yi... haka darajar nasarar take raguwa idan ta fito. Koyi aiki a shiru.

4. Tsari a harkar kudi.
A zahirin gaskiyar duniya... girmamawa tana bin namijin da aljihunsa yake da tsari ne.

5. Tsaya akan tsari.
Idan baka da tsari ko doka akan rayuwarka... mutane zasu dauko tasu dokar su dora a kanka.

6. Girmama kowa, amma kar kaji tsoron kowa.
Asalin karfi... nutsuwa ne. Hayaniya rauni ne a boye.

7. Daukar alhaki.
Namijin da yake yawan dora laifin kasawarsa akan wani, a tsaye yake. Baya taba cigaba.

8. Cigaba da gina kanka.
Asalin girmanka, shine kokarin da kake yi na gyara kura-kuranka a boye.

9. Kare nutsuwarka.
Namijin da kowa zai iya jefa shi a rudani, baya zama abin dogaro.

10. Tafiya da alkibla.
Namijin da ya san inda ya dosa... kowa yana bashi hanya ya wuce.

Fushi. Gajiya. Rudani. Koyi hadiye su a gaban mutane.
Ba wai don baka da zuciya ba.
Sai dai Saboda duniya tana kallon yadda kake daukar matsi ne kafin ta baka girma.

Koyi nutsuwa a lokacin da komai yake a cabe maka.
Yana sa ka zama mai hatsari.

UMAR ALIYU DAHIRU

26/04/2026

Yanxu a wasu Jahohin an rigada an chanza musu Tunanin Yanci, Demokradiya da kuma Siyasa.

Wasu kawai jira suke ace musu ga wanda Gomna ya cire...... Shine Zai gaje shi a matsayin Gomna.....

Ita Kujerar Gomna an zamar dashi na Gado kenan! Sai abunda ake ce muku ga wanda Gomna ya fitar..... kumafa ba zaben akeyi ba mussamman wasu Jahohin. Kawai Nadi akeyi...

Mutum Ya gama Wa'adinshi, Anma a Dole sai yakawo muku wanda zai gajeji, Saboda Gudun Zirga zirga a kotu da Efcc.

Ita Demokradiya fa Yanci ce, itace ta Haifi Siyasa, shiyasa akace Ayi Zabe. Saboda ku zabi abunda Ranku yake so Don Ya jagorance ku, Ba Abunda wani yake so ba.

26/04/2026

Duk maccen da ta yarda Namiji yana sonta to ta yaudari kanta.

Shi namiji yana son abin da yake wajen mace ne, ba ita macen ba.

Misali: idan namiji yana son mace mai ilimi idan ya samu to zai makale mata. Idan kuma yana son abinci mai dadi idan ya samu wanda ta iya, shikenan ya ga wajen zama. Haka idan yana son kyakkyawa ce, idan ya samu ba wanda ya isa ya kuce ta bayyi fada da shi ba.

Sai yasa idan namiji ya samu abin da yake so a wajen mace, zai zauna yayi likimo, ai ta cewa wance ta asirce shi, ya ce naji din 😂 shi dai ba yana samun abin da yake so ba? Oho muku.

Kaga shi wannan kudin yake bukata a wajenta kuma ya samu sai ya kara gaba, da ace yasan kudin ta ne, ma’ana tana da hanyoyin samin kudi. To zai tsaya sai sun yi aure, ya azurta sannan ya fece, amma da yasan iya wannan kudin ne, da ya cafke su sai ya kara gaba.

Anan kuma ina son maza in ba ku shawara, ku rinka lura idan kana son gane macen da ke sonka, akwai wasu abubuwa da zai bayyana a tare da ita na dabi’u.

Na farko; Duk macen da ba ta damu da kudin ka ba, tana sonka. Macen da za tai ta nuna maka ita fakiriya ce, kai komai sai ka mata, to karya take amfani take da kai wajen habaka jarin ciyar da wani, don a gefe tana can tana nunawa wanda take so tana da kudi. Domin mata yan gata ne, a ko wane gida mace tana samun tallafi daga magabatanta iya level din arzikin gidan su.

Na biyu, Macen da baza ta kiraka ba sai ka neme ta, idan kayi korafi akan bata damu da taji ya kake ba, sai ta baka uzurin ai tana tunanin aiki ne yayi maka yawa. Karya take, mata a hankalin su idan suna son abu basa baza uzurin wai ba su ganshi ba ko basu ji shi ba. Ina ruwanta da busyn ka kawai ita ta kira ta ji ya shiga ma, sai taji dadi a zuciyarka. Kuma idan baka daga ba ai maka korafi, kullum ita cikin maka korafi

Na uku…. Na cigaba ko na bari sai wani lokaci? Bari na bari amma akwai kusan matakai 12 da zaka gane mace na sonka ko ba ta sonka.

Ke kuma Mace, duk namijin da k**e tare dashi ba ki ga wasu a lamonin 7 ba, shi na

TARIHIN AISHA LEMU.Aisha Bridget Lemu, Shahararriyar marubuciyar litattafan addinin Musulunci ce haifaffiyar Birtaniya K...
21/04/2026

TARIHIN AISHA LEMU.

Aisha Bridget Lemu, Shahararriyar marubuciyar litattafan addinin Musulunci ce haifaffiyar Birtaniya Kuma mazauniyar birnin Minna a taraiyar Najeriya. An haifeta a 1940, Kumar ta karbi musulunci a 1961, ta rasu a garin minna na jahar Neja ranar 5 ga Janiru na 2019.

Lokacin da tana yar shekara goma sha uku (13), ta fara yin tunani na canza addini kuma ta fara nazarin sauran addinai, cikinsu har da addinin Buddha da na Hindu.

Ta yi karatu a Jami’ar London, a makarantar koyan al’adu da harsunan kasar sin da Africa wato school of oriental and African studies (SOAS), a inda ta mai da hankalinta ga tarihin kasar Sin, da al’adun su.

Ta hadu da dalibai Musulmai a wannan Jami’a ta (SOAS) waɗanda s**a ba ta littattafan addinin musulunci ta ke karantawa, kuma ta karbi Musulunci a Cibiyar Al’adu ta Musulunci a shekarata 1961,

A shekarar farko ne a kartunta ta bada gudunmawa wajen samar da kungiyar dalibai Musulmai a SOAS, a jami’ar ta London kuma itace sakatariyar kungiyar ta farko a makarantar.

Bayan ta kammala karatun ta daga SOAS, Aisha ta tafi karatun digiri na biyu don koyan turanci kuma a lokacin ne ta hadu da mijinta, Sheikh Ahmed Lemu, wanda yake karatunsa a wata koleji a Jami’ar London, kuma ya shiga cikin ayyukan Musulunci a makarantun da suke yankin na london.

Bayan da ta samu takardar shaidar gama digirinta na biyu a makarantar, ta koma Kano a watan Agustan, a shekara ta 1966 ta fara koyarwa a Makarantar Nazarin Larabci a, inda Sheikh Ahmed Lemu ya yi aiki a matsayin shugaban makarantar.

Sun yi aure da Sheikh Ahmed Lemu a watan Afrilun shekara ta 1968, Aisha ta zama matarsa ta biyu.

Daga baya sai ta koma Sokoto don ta zama shugabar makarantar Kwalejin ‘Yan mata ta gwamnati a sokoto.

Sheikh Ahmed Lemu shine babban kadi na kotun daukaka kara na shari’a a Nija lokacin da aka kafa ta a shekara ta 1976, Aisha kuma ita ce shugabar babbar makarantar malamai mata a Minna har zuwa 1978.

Ma’auratan biyu sun kafa kungiyar Ilimin Musulun

Alhamdulillahi
21/04/2026

Alhamdulillahi

11/01/2025

If you want to test some one character gives him respect

11/01/2025

D

O Allah, please make my 2025 a happy year full of halal rizq, happiness, good memories, better health and strengthened I...
31/12/2024

O Allah, please make my 2025 a happy year full of halal rizq, happiness, good memories, better health and strengthened Imaan. Ameen

31/12/2024

"I stand by my comment. I cannot be threatened," Mohammed said on Channels Television's 2024 Year-End Review.

Address

Gombe

Telephone

+2348033896255

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Auwaluje Bawan Allah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Auwaluje Bawan Allah:

Shortcuts

Share